GUDUNMOWAR SOSHIYAL MIDIYA WURIN CIGABAN ADABIN BAHAUSHE

 


Soshiyal midiya wacce ake fassarawa da ‘kafafan sada zumunta na zamani’ ta taimaka wajen tallanta adabin Bahaushe ta hanyoyi da dama, kama daga rubututtuka waɗanda suka haɗa da saƙonni, gajerun labarai, waƙoƙi har izuwa wasanni kwaikwayo. Ta kuma ƙara fito da al'adun Hausawa fili, tare da tagomashin samar da rana guda kacokan domin bajakolin yaren Hausa a sanadin soshiyal midiya.

 

Zuwan soshiyal midiya ya haɓaka yawan rubututtuka da Hausawa da sauran ma'abota aiki da yaren Hausa suke yi. Domin kuwa a kullum, mutane suna amfani da waɗannan kafafan sadarwa wajen aikawa da karɓar saƙonni cikin harshen Hausa, musamman a kafar sadarwa ta WhatsApp da Facebook Messenger. Hakanan, an samu, kungiyoyi da zaurukan wanda suke da alaƙa da adabi da suke amfani da soshiyal midiya wajen gudanar da kuma haɓaka shirye-shiryensu. Misali, akwai gasar rubutacciyar waƙa da ake a dandalin sada zumunta na Facebook da akewa take da 'Asabe' wanda yake zaburar da mutane wajen rubuta waƙoƙi a kowacce Asabar, da sauran makamantan shirye-shirye irin wadanan.

 

Bugu da ƙari, a yanzu, dandalin sada zumunta na Facebook, wanda shine babbar kafar sada zumunta ta duniya yana da kimanin mutane biliyan uku (Data Reportal 2022), kuma akan wannan kafa, akwai yaren Hausa cikin jerin yarika da mutum zai iya amfani dasu wajen sarrafa wannan manhajja ta Facebook, kamar yadda zai iya amfani da Turanci, Larabci, Faransanci da sauran manyan yare da ake amfani dasu a duniya. Wannan ya ƙara ɗaukaka adabin Hausa a idon duniya baki ɗaya. Hatta waɗanda basu san menene yaren Hausa ba, sanadiyyar soshiyal midiya a yau, samun wayewar kai akansa. Hakanan akan ragowar waɗansu daga cikin saura kafofin za ka samu yaren Hausa ya samu gindin zama.

 

Wani abin alfahari da soshiyal midiya ta haifarwa adabin Hausa a yau shine rana ta musamman da aka ƙirƙira a dalilin kafafan sada zumunta domin tinawa da Harshen Hausa a duniya, wato 26 ga watan kowanne Agusta. Hakan ya janyo hankalin mutane a duniya da dama akan adabin Hausa ta yadda Hausawa da suaran masu amfani da harshen Hausa suke bajakolin maganganu cikin hikima, da amfani da karin magana da waƙe da habaici da zambo da sauran fannoni na adabin Hausa domin nuna bajinta da alfahari da harshen Hausa a wannan ranar. Tabbas, wannan abin akwai banƙaye acikinsa, kuma ba a nan kawai ya tsaya ba, ƙasashe irinsu su Najeriya, Ghana, Chadi, Nijar suna haɗa taruka na musamman domin gabatar da jawabai da maƙaloli akan muhimmancin adabin Hausa. Wannan duka yana faruwa sanadiyyar wata gaɓara da ta faro ne daga soshiyal midiya.

 

Sannan soshiyal midiya tana taka muhimmiyar rawa wajen koyo da koyarwa na adabin Malam Bahaushe. Akwai shafuka yanzu waɗanda aka ƙirƙiro akan kafafan sada zumunta na zamani domin koyar da wasu fannoni na adabin Hausa. Sannan akwai masana akan adabin Hausa suma da suke amfani da shafukansu wajen daɗa ilimantar da mutane akan abubuwa daban-daban domin ƙara wayarwa da al’ummar Hausawa kai. Hakanan kuma, akwai zauruka da ake ƙirƙira musamman a kafar sada zumunta ta WhatsApp domin koyar da adabi da kuma gudanar da wasu shirye-shiryen domin haɓaka adabi. Ya isa misali zauren WhatsApp na kungiyar marubuta ta ƙasa reshen jihar Kano (ANA KANO), da sauran zauruka da dama waɗanda ake buɗewa domin koyar da rubutacciyar waƙa, da waɗanda ɗaliban adabin Hausa suke buɗewa domin taimakawa nazarinsu, da sauransu.

 

Waɗannan, dama sauran abubuwa waɗanda suka haɗa shirye-shirye na musamman akan soshiyal midiya lokaci bayan lokaci waɗanda suke ƙara karkato da hankalin mutane izuwa kan adabin Hausa, tare da taimakawa matuƙa gaya wajen ƙara tallata ƙungiyoyi da mutane da suke da alaƙa da adabi, hatta ƙungiyar marubuta ta ƙasa (ANA) ta samu tagomashin tallata ayyukanta da kuma gudanar da shirye-shiryenta ta hanyoyi mabanbanta akan soshiyal midiya tare da adana bayanai domin waɗansu su amfana ko kuma su kalla ko saurara alhali basa inda ake gabatar da shirye-shiryen. Wannan duka sun samu ne sanadiyyar soshiyal midiya.

Comments

Popular posts from this blog

'SANIN MANUFAR RAYUWA SHI NE RIBAR ZUWA DUNIYA' NA KHADEEJAH MUHAMMAD DAYYEEB

THE END OF POVERTY BY JEFFREY SACHS

TOWARDS SUSTAINABLE WASTE MANAGEMENT APPROACH IN KANO METROPOLIS: LESSONS FROM MUSLIM CITIES