TASIRIN MAƘOTA NA GARI
Amon ‘labbaikallahumma labbayka’ ne yake tashi a karo na uku daga wayar Alh. Bello, cikin hanzari ya ɗ aga “Mal. Auwal afuwan!” Ashe Mal. Auwal ne ma ƙ ocinsa zusu je ɗ aurin auren ladanin unguwarsu a yau Asabar wanda za a yi ƙ arfe 11ns. Fitowar Alh. Bello kenan, ya tadda Mal. Auwal zaune cikin motarsa yana jiransa. Fara tafiyarsu ke da wuya Alh. Bello yace “Akwai bu ƙ atar na sayi wani abu a danja domin ban ƙ arya ba. Amarya tana bacci da ƙ yar ta samu tace min a dawo lafiya cikin magagi”. Tausayin Alh. Bello ne ya kama Mal. Auwal domin shi kuwa tun da suka tashi sallar Asuba matarsa Zainabu ta saka alarm , ta tashi da wuri, ta tashe shi yayi wanka inda ta riga ta kai masa ruwan wanka bayi. Fitowarsa ke da wuya, ya riski bu ɗ a baki yana jiransa. Cikin nisha ɗ i suka karya suna hira daga bisani ya fara kiran Alh. Bello. Tabbas akwai tawaya cikin kulawar da Alh. Bello yake samu daga uwar ɗ akinsa Bikisu. Haka Mal. Auwal yayi ta sa ƙ e-sa ƙ e, tinanin yanda zai taimakawa abokinsa d...