'SANIN MANUFAR RAYUWA SHI NE RIBAR ZUWA DUNIYA' NA KHADEEJAH MUHAMMAD DAYYEEB

 


Littafi ne mai shafuka 66 wanda Markazut-Tarbawi Al-Islamee, Kano, Nigeria suka wallafa shi wanda yake cike da wa'azi mai shiga zuciya da kuma cikakkiyar tinatarwa cikin taƙaitattun kalmomi a kan manofofin rayuwarmu ta duniya, da kuma yadda za mu ribace ta.

Malama Khadeejah ta buɗe littafin ne da bayani a kan tsarin matakan rayuwar ɗan adam inda ta kasa ta zuwa matakai guda huɗu

1.      Rayuwar ɗan adam a cikin mahaifiya

2.     Rayuwar ɗan adam a Duniya

3.     Rayuwar ɗan adam a barzahu, da kuma

4.     Rayuwar ɗan adam a Lahira

 

Rayuwar Cikin Mahafiya

Malama Khadeejah ta yi bayani musamman abin da ya shafi ma'anar wannan rayuwar da kuma abubuwan da suke faruwa kamar yadda Manzon Allah SAW ya yi bayani tun ɗan adam yana maniyyi, da kwanakin da yake ɗauka ya zama gudan jini, gudan tsoka, har zuwa a busa masa rai, da ma lokacin da za a haife shi tare da darussan da suke ciki; musamman irin taƙaitaccen lokacin da ɗan adam yake a wannan mataki na rayuwa da bai wuce ƴan watanni ba.

 

Rayuwar Duniya

Matakin na biyu kuma wato rayuwar duniya, Malama Khadeejah ta yi jawabi tare da jan hankali a kan irin yadda Allah SWT ya umarce mu da mu gudanar da ita, cikin neman kusanci zuwa gareshi, ta hanyar biyayya ga dokokinsa da ya shimfiɗa mana ta hanyar manzonsa, Annabi Muhammad SAW. Ta kuma maida hankali matuƙa wajen ƙoƙarin fahimtar da mai karatu cewa rayuwarsa ta duniya, wata jarrabawa ce da Allah yake masa domin tantace gaskiyar imaninsa, ta yadda ɗan adam zai maida dukkan ayyukansa, a matsayin hanyoyin bauta ga Ubangiji. Da kuma nisantar saɓa masa tun daga kan nema, mu'amala, da kuma kula da ibada. Ta kuma ja hankali a kan lalle kada mu shagala da abubuwan da za su ɗauke hankalinmu wajen bautawa Allah yayin gudanar da taƙaitacciyar rayuwar duniya, wacce ba komai ba ce idan mutum ya haɗa ta da ta Lahira.

 

Rayuwar Barzahu

Rayuwar barzahu ita ma ta yi cikakken bayani a kan ta tare da kawo hadisai da ayoyi kasancewar ta madagata (rayuwar kabari) kafin isa zuwa Lahira. A wannan rayuwar mutum yake haɗuwa da mala'iku da za su yi masa tambayoyi wanda amsa za ta fito gwargwadon yadda bawa ya mu'amalanci addininsa a duniya. Ga wanda ya bi Allah, ya kuma nisanci saɓa masa, zai samu nasarar tsallakewa tare da samu yalwa a kabarinsa da kuma fara samun tagomashi na rahama daga Allah SWT sakamakon ayyukan alheri da ya aikata. Kafiri, da munafiki, da mujirimi kuwa, za su gaza amsawa, take kuma za su fara fuskantar matsin kabari da kuma azaba har a tashi alƙiyama.

Daga cikin nau'in munafurci da Malama Khadeejah ta zayyana mana akwai:

1.      Faɗin imani a baki tare da saɓa wa hakan a zuciya

2.     Ƙaryata Annabi SAW ko kuma wani abu da ya zo da shi; ta yadda mutum zai ji cewa waɗansu tabbatattun hukuncin Musulunci ba adalci ba ne ko kuma jin saɓa wa  dokokin Allah ba wani abu ba ne

3.     Yin izgilanci ga sha'anin imani ko masu imani

4.     Toshe hanyar cigaban Musulunci

5.     Jin daɗi yayin da wani abu mara daɗi ya samu muminai

Waɗannan na daga cikin ɗabi'un munafiki da ya kamata mutum ya yiwa kansa katangar ƙarfe daga afka musu domin gujewa fushin Allah SWT.

 

Shi kuma fajiri shi ne mai yawan aikata manyan laifuka a bayyane kuma cikin izgilanci. Kuma kamar yadda muka gani a sama duka suna faɗawa cikin waɗanda ba za su ci nasarar amsa tambayoyin kabari ba, duk da cewa, azaba tana komawa gwargwadon yadda bawa ya saɓa wa Allah SWT matuƙar bai yi kafirci ba.

 

Rayuwar Lahira

Sai kuma rayuwar Lahira, inda Malama Khadeejah ta maida hankali kacokan a kan Aljanna da kuma ni'imomin da suke cikinta, musamman abin da ya shafi dawwama da kuma abubuwan jindaɗin da suka sha ban-ban da abin da muka sani anan duniya. Malama Khadeejah ta yi jawabi cewa rayuwar Aljanna ita ce rayuwar Lahira domin kuwa wutar Jahannama, ba rayuwa ake a cikinta ba kuma ba mutuwa ake ba, kamar yadda Allah ya yi jawabi cewa – “Ba a mutuwa a cikinta kuma ba a rayuwa.” Tabbas duk mai karatu idan ya fahimci irin tanadin ni'imomin da Allah SWT ya yiwa bayinsa na gari a Aljanna, babu makawa, ya sake ɗaura ɗaramar kyautata tsakaninsa da mahaliccinsa.

 

Lokacin da Malama Khadeejah ta dawo kan bayanin akan wutar Jahannama da irin narkon dake tare da ita, dole zuciyar mai karatu ta raurawa tare da sake nisanta aikin da zai jefa bawa cikinta. A cikin hikimar Allah SWT kuma ya kasance Lahira gida biyu gareta, ko dai Aljanna, ko wuta, don haka duk bawan da ya shiga wuta, Malama Khadeejah ta nusasshemu da cewa shi ya zaɓa, domin an katse masa hanzari ta hanyoyi da dama musamman ta wuraren guda biyu da ta yi mana jawabi kamar haka:

1.      Aiko manzo da saƙon Allah, da kuma

2.     Gatan iyaye: wanda Allah ya yiwa bayinsa cikin hikimarsa.

Kuma, Allah ya tsara cewa ba zai tuhumi bawa ba face ya kai shekaru balaga, wanda kafin nan, gatan tarbiya da iyaye za su ba shi ya ishe shi fahimta waye Allah kuma ta ya ya zai bauta masa.

 

Daga ƙarshe Malama Khadeejah ta yi tanbihi ta hanyar dubayya ga abubuwan da suke kamanceceniya tsakanin rayuwar da ɗan adam yake yi a cikin mahaifiya da kuma rayuwar barzahu, hakanan tsakanin rayuwar Duniya da ta Lahira.

 

Tabbasa mai karatu ba zai taɓa wadatuwa da irin wannan gajerin lattafi ba mai cike da tasiri mai girma wajen ƙoƙarin juya akalan al'umma zuwa abin da zai fisshe su Duniya da kuma Lahira. Haka nan littafin ya rubutu cikin bin ƙa'idar rubutun Hausa wanda hakan zai ba wa mai karatu damar karanta shi cikin sauƙi, Allah Ya saka wa Malama Khadeejah da mafificin alherinsa, amin!


Comments

Popular posts from this blog

FAREWELL MESSAGE - UNDERGRADUATE

THIRTY-MINUTE JOURNEY WITH HONEYBEE: A LESSON FOR REFLECTION - A REVIEW

THE END OF POVERTY BY JEFFREY SACHS